Me zai faru idan INEC ta soke rijistar jam'iyyar ADC?

📌 Diğer 📰 Nigeria 🕐 3 saat önce
Me zai faru idan INEC ta soke rijistar jam'iyyar ADC?

Masana siyasa na ganin wannan hukuncin na iya kawo tsaiko ga jam'iyyun adawa a ƙasar, amma idan suka ɗauki matakin da ya dace da wuri za su yi wa tufkar hanci.

A Najeriya, ana ta cece-ku-ce kan wani hukuncin kotun da ya umurci hukumar zaɓe ƙasar, INEC ta soke rijistar ɗaya daga cikin manyan jam'iyyun adawa ADC, da wasu guda huɗu.

Kotun tarayyar ƙasar ta ce jam'iyyun da hukuncin ya shafa sun gaza cika sharuɗɗan da kundin tsarin mulki ya tanada, na samun aƙalla kashi 25 cikin 100 na ƙuri'un da aka kaɗa a zaɓuka bayan yi musu rijista, ko kuma lashe aƙalla wata kujera ɗaya.

Jam'iyyun da hukuncin ya shafa su ne Accord, APP, AA, ADC da ZLP. Ƙungiyar Tsofaffin Ƴan Majalisu ta Ƙasar ne ta shigar da ƙarar.

Sai dai rahotanni sun ce kotun ɗaukaka ƙara da ke Abuja ta dakatar da aiwatar da hukuncin inda ta umarci INEC da kada ta ɗauki wani mataki na soke rajistar jam'iyyun har sai an kammala sauraron ƙarar da suka shigar kan hukuncin da kotun ƙasa ta yanke.

Faisal Kabir mai magana da yawun jam'iyyar ADC ya ce "INEC ce ta shigar da ƙorafin a kotun ɗaukaka ƙara kuma ta tuntuɓe su kafin shigar da ƙarar".

Jam'iyyun dai sun yi watsi da hukuncin tare da shan alwashin ƙalubalantar matakin, inda suka ce hukuncin ya ci karo da abin da yake a zahiri.

A hukuncin da mai shari'a Peter Lifu, ya yanke a babbar kotun tarayya da ke Abuja, ya umurci INEC da kada ta bari waɗannan jam'iyyu su shiga duk wasu zaɓuka masu zuwa, ciki har da babban zaben shekarar 2027, sai dai idan sun cika duk wata ƙa'ida da doka ta tanada.

Barista Aminu Abdulrasheed, ya ce kotun ta yi la'akari ne da kundin tsarin mulki sashe 225(A) da kuma sashe na 25(4) na kundin dokokin zaɓe na 2022.

Yanzu za ku iya samun labaran BBC Hausa kai-tsaye a wayoyinku.

Ya ce sashen ya ba hukumar zaɓe iko ta cire jam'iyyar da ka gaza cika sharuɗɗan, wanda saboda shi ne wasu tsoffin ƴan majalisar wakilai ta ƙasar suka shigar da ƙara a kai.

"Hukuncin ya yi daidai da duk tanade-tanaden da ke cikin kundin tsarin mulki na 1999," in ji Lauyan da ke nazari kan harkokin da suka shafi siyasa da lamuran yau da kullum.

Sai dai Faisal ya ce ita kanta INEC na ganin za a ɓata mata shiri idan aka yi wannan hukuncin yanzu, shi ya sa ta ƙalubalanci matakin inda za a ci gaba da shari'ar da ke gabanta.

Masana siyasa na ganin wannan hukuncin na iya kawo tsaiko ga jam'iyyun adawa a ƙasar, amma idan suka ɗauki matakin da ya dace da wuri za su yi wa tufkar hanci.

Farfesa Kamilu Sani Fagge, masani harkokin siyasa na ganin irin waɗannan abubuwan da ke faruwa na nuna yadda ake yi wa fannin shari'a katsalandan.

"Idan kotu na ba da hukunce-hukunce da ke cin karo da dokokin, to gaskiya hakan na nuna dimokraɗiyyarmu na da matsala," in ji shi.

Barita Abdulrasheed ya ce: "Idan aka yanke hukunci a shari

📌 Kaynak

Bu haber XML kaynağından derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.

Orijinal haberi oku →
📱
News AI World — Mobil uygulama
Bu haberleri 45 dilde, anlık çeviriyle cebinde. Erken erişim için Gmail adresini bırak.
← Tüm haberlere dön