Yadda kawo ƙarshen yaƙin Iran ya fallasa raunin Amurka

📌 Diğer 📰 Nigeria 🕐 3 saat önce
Yadda kawo ƙarshen yaƙin Iran ya fallasa raunin Amurka

Yarjejeniyar kawo ƙarshen yaƙi da sake buɗe mashigar Hormuz ta bar ɓangarorin a daidai matakin da suke sa'o'i 24 kafin fara yaƙin - sai dai yanzu dubban mutane sun mutu.

Wannan yaƙin ya kasance wani babban kuskuren manufofin ƙasashen waje na Shugaba Donald Trump - ya zuwa yanzu.

Hakan ya rage irin kallon tsoron da abokan gaban Amurka ke yi ma ta.

Ta lalata dangantakarta da ke tsakaninta da shugabannin ƙasashen larabawa masu arzikin man fetur na yankin Gulf, lamarin da zai ɗauki dogon loakci kafin a iya dawo da shi yadda ya ke a baya.

A bayan fage, jami'an ƙasashen sun riga sun fara magana game da karkatar da mubaya'arsu, da kuma wajibcin neman hanyoyin zama tare da Iran, makwabciyarsu da ke ketaren ruwa. Ƙasar China za ta sa ido sosai yayin da Amurka ta ɓarnatar da makamanta da ke da wahalar samu ta kuma fuskanci gaskiyar rashin ƙarfin ikonta.

Idan har ba a samu wani cikas ba ana sa ran yarjejeniyar za ta kawo ƙarshen yaƙin da ya samo asali daga yadda Amurka da Isra'ila suka yi kuskure wurin raina ƙarfin maƙiyansu da ke Tehran. Hakan dai zai taimaka wruin kwantar da hankalin mutanen da yaƙin ya hargita musu rayuwarsu.

Yarjejeniyar za ta sake buɗe mashigar Hormuz, in ji Trump, tare da rage matsin lamba kan tattalin arzikin duniya da kuma haƙiƙanin rayuwar ɗaruruwan miliyoyin mutanen da ke cikin mawuyacin hali a duniya.

An kashe dubban mutane a Gabas ta Tsakiya. An lalata gidaje da wuraren kasuwanci. Samar da takin zamani da ya dogara da kayan da ake jigila ta mashigar na iya nufin mutane da ke ƙasashe matalauta za su yi fama da yunwa daga baya a cikin shekara, inda ƙasashen Afirka da ke yankin kudu da hamadar Sahara ke cikin haɗari.

Yarjejeniyar ba tazaman lafiya ba ce. Cikakkiyar yarjejeniyar, wanda masu shiga tsakani suka ce yana ɗauke da sharuɗɗa 14 akan shafuka biyu, har yanzu dai ba a wallafa ta ba. Sai dai baya ga sake buɗe mashigin ruwan, yarjejeniyar fahimtar juna ta ƙara tsawaita tsagaita wuta tare da dage takunkumin da sojojin ruwan Amurka suka yi wa tashar jiragen ruwa na Iran.

Ta dai ƙara tura muhimmin batu da ke cike da sarƙaƙiya zuwa zagayen tattaunawa na gaba . Wannan ajandar dai za ta haɗa da makomar shirin nukiliyar Iran da kuma matakin sassauta takunkumin da za ta samu domin samun sassauci.

A ƙarshe, an shata layi a ƙarƙashin yaƙin da Amurka da Isra'ila suka fara a ranar 28 ga Fabrairu.

Yanzu za ku iya samun labaran BBC Hausa kai-tsaye a wayoyinku.

Yanzu dai a mayar da hannun agogon baya zuwa ranar 27 ga watan Fabrairu, yayin da sojojin Amurka da na Isra'ila ke shirin kai farmaki, suna shirya makaman jiragensu, tare da yiwa ma'aikatansu bayani, da kuma tsara wuraren da makamansu za su kai wa hari.

A Geneva, Iran da Amurka sun shiga cikin abin da aka bayyanawa duniya a matsayin muhimmiyar tatt

📌 Kaynak

Bu haber XML kaynağından derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.

Orijinal haberi oku →
📱
News AI World — Mobil uygulama
Bu haberleri 45 dilde, anlık çeviriyle cebinde. Erken erişim için Gmail adresini bırak.
← Tüm haberlere dön