'Yarjejeniyar Iran da Amurka ta ƙunshi kafa gidauniyar biliyan 300 ga Tehran'
Wannan shafi ne da ke kawo muku abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya na ranar Laraba 17 ga watan Yuni 2026.
Jagororin jam’iyyun adawa na ci gaba da bayyana farin cikinsu kan hukuncin da kotun ƙoli ta yanke na dakatar da aiwatar da hukuncin da kotun tarayya ta yanke na soke rajistar wasu jam’iyyun siyasa a ƙasar.
Kotun ƙolin da ke zamanta a Abuja ta bayar da umarnin dakatar da aiwatar da hukuncin da Alkali Peter Lifu ya yanke, wanda ya umarci hukumar zaɓe ta ƙasa INEC da ta soke rajistar jam’iyyun ADC da APP da AA da AP da ZLP.
A hukuncin nata, kotun ta zargi alƙalin da saɓa wa umarnin da ta bayar tun farko, inda ta ce ya yi watsi da umarnin dakatar da sauraron shari’ar da kuma nuna halin girman kai a tsarin shari’a.
Kotun ta bayyana matakin a matsayin mafi girman raini ga tsarin shari’a tana mai cewa alƙalin ya nuna halin rashin ladabi a aikin shari’a bisa ci gaba da shari’ar duk da umarnin da aka riga aka ba shi.
A sakamakon haka, kotun ɗaukaka ƙolin ta amince da buƙatar dakatar da aiwatar da hukuncin, tare da umartar cewa a dakatar da duk wani mataki na aiwatar da hukuncin har sai an kammala sauraron ƙarar gaba ɗaya.
A baya dai, kotun babbar tarayya ta umarci INEC da ta soke rajistar jam’iyyun biyar, bisa zargin gazawarsu wajen cika sharuddan ƙundin tsarin mulki da ke ba su damar ci gaba da kasancewa a matsayin jam’iyyun siyasa a ƙasar.
📌 Kaynak
Bu haber XML kaynağından derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.
Orijinal haberi oku →