Me ya janyo musayar yawu tsakanin Rarara da Davido?

📌 Diğer 📰 Nigeria 🕐 3 saat önce
Me ya janyo musayar yawu tsakanin Rarara da Davido?

Wata cece-ku-ce ta ɓarke a shafukan sada zumunta tsakanin fitattun mawaƙan Najeriya biyu na Davido da Rarara.

Wata cece-ku-ce ta ɓarke a shafukan sada zumunta tsakanin fitattun mawaƙan Najeriya biyu Davido da Rarara.

A ranar Talata da daddare ne dai fitaccen mawaƙin siyasa a arewacin Najeriya, Dauda Kahutu Rarara ya wallafa wani bidiyo a shafukansa na sada zumunta, inda a ciki ya soki fitaccen mawaƙin Kudancin ƙasar David Adedeji Adeleke da aka fi sani da Davido.

Davido dai ya bayyana ne a wani bidiyon waƙa da ya gudanar a bikin shirye-shiryen fara gasar Kofin Duniya, sanye da riga mai ɗauke da tutar Najeriya rubuce da sunayen yara ɗaliban da aka sace a jihar Oyo.

A watan da ya gabata ne dai wasu mahara masu iƙirarin jihadi suka kai hari makarantar yara a jihar Oyo tare da sace ɗalibai da wasu malamansu, lamarin da ya tayar ƙura da ke ci gaba da janyo wa gwamnatin Najeriya suka daga ƴan ƙasar.

Bayyanar da Davido ya yi sanye da rigar da ke ɗauke da sunayen yaran da aka sace a jihar Oyo a bikin shirye-shiryen fara gasar Kofin Duniya, ya ce ya yi ne domin nuna goyon baya ko tausayawa ga ɗaliban.

Sai dai a nasa ɓangare, Rarara na ganin matakin na Davido tamkar kunce wa gwamnatin Bola Tinubu - da yake goyon baya - zane ne a kasuwa.

Ba dai wannan ne karon farko da ake samun taƙun saƙa tsakanin fitattun mawaƙan Najeriya ba, lamarin da wasu masana ke alaƙantawa da 'hassadar mawaƙa'.

Cikin bidiyon nasa da ya yi wa take da martani, mai tsawon minti 11, Rarara ya yi magana kan batutuwa masu yawa, sai dai ya fara ne da batun na Davido.

Yanzu za ku iya samun labaran BBC Hausa kai-tsaye a wayoyinku.

Ya bayyana matakin na Davido a matsayin ''nuna goyon bayan ƙungiyar Ansaru'' ta masu iƙirarin jihadi, waɗanda ake zargi da sace ɗaliban na jihar Oyo.

''Ta yaya za ka ɗauki sirrin Najeriya na cikin gida, ka kai shi fagen duniya'', in ji shi.

Rarara ya zargi Davido da siyasansar da matsalar tsaro, bayan da ya yi zargin cewa ƙanin mahaifin Davido na takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar Accord Party.

Rarara ya ce batun tsaro abu ne da bai kamata a yi masa karan-tsaye ba.

''Ya kamata ka buƙaci a yi maka bayanin ina aka tsaya, da matakin da ake kai yanzu kafin ka yi magana a kai'', a cewar mawaƙin siyasar.

Rarara ya yi ikirarin cewa mayaƙan Ansaru sun sace ɗaliban Oyo ne da nufin a sako muku manyan shugabanninsu da aka sace.

''Sun ce ba za su saki yaran ba, har sai an sakar musu jagororinsu, amma shugaban ƙasa da shugabannin tsaro suka ce ba za a saki shugabannin ƙungiyar ba, kuma kuma suke ƙoƙarin ƙwato daliban'', kamar yadda ya yi iƙirari.

Mawaƙin ya kuma zargi wasu ƴansiyasa da amfani da matasa masu amfani da shafukan sada zumunta wajen yayata batun matsalar tsaro.

A na

📌 Kaynak

Bu haber XML kaynağından derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.

Orijinal haberi oku →
📱
News AI World — Mobil uygulama
Bu haberleri 45 dilde, anlık çeviriyle cebinde. Erken erişim için Gmail adresini bırak.
← Tüm haberlere dön