Shin dattawa ne suka mamaye siyasar Najeriya?
Tinubu ya girmi gwamnan da ya fi ƙarancin shekaru da shekara 26, sannan ya girmi gwamnonin da suka fi kowa shekaru da shekara bakwai.
Duk da cewa matasa su ne mafi rinjayen al'umma a Najeriya, har yanzu dattawan da suka haura shekaru 45 a duniya kuma suka daɗe suna taka rawa a harkokin mulkin ƙasar ke ci gaba da riƙe manyan muƙaman siyasa.
Yawancin waɗanda suka daɗe ana damawa da su sun riƙe muƙamai ne tun suna matasa, amma yanzu ana ganin sun ƙi ba matasa dama. A shekarar 2018, matasa sun yi ta fafutukar ganin an samar da dokar "Not Too Young To Run" da za ta ba matasan damar riƙe manyan muƙaman siyasa.
Sai dai ana ci gaba da muhawara kan adadin shekarun da ya kamata a ƙayyade na matasa, inda wasu ke ganin duk mutumin da ya zarta shekaru 35 ya wuce shekarun da za a kira shi da" matashi" yayin da wasu ke cewa shekaru 40.
Wasu daga cikin dattawan da aka daɗe ana damawa su sun yi gwamnoni, ministoci, sanatoci na tsawon shekaru, lamarin da ya sa ake ganin tsarin da ake tafiya a kai ya taƙaita damar sabbin jini shiga harkokin shugabanci.
Wannan ya sa ake ci gaba da tambayar ko siyasar Najeriya na bai wa matasa damar hawa manyan madafun iko, ko kuwa dattawan ne za su ci gaba da jan zarensu a shekaru masu zuwa, idan aka yi la'akari da waɗanda suke kai yanzu?
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, na da shekaru 74 a duniya. An haife shi ne a ranar 29 ga Maris, 1952.
Kafin hawansa kujerar shugaban ƙasa a shekarar 2023, Tinubu ya yi gwamnan Jihar Legas daga 1999 zuwa 2007, inda daga bisani ya zama Sanata kuma ya kasance ɗaya daga cikin fitattun masu tasiri a siyasar Najeriya tsawon shekaru.
Mataimakin shugaban ƙasar, Kashim Shettima, kuwa an haife shi a ranar 2 ga Satumba, 1966. A yanzu yana da shekaru 59 a duniya.
Kafin zama mataimakin shugaban ƙasa, Shettima ya yi gwamnan jihar Borno na wa'adi biyu tsakanin 2011 da 2019, sannan ya wakilci Borno ta Tsakiya a Majalisar Dattawa.
Duk da cewa shekarunsa ba su kai na shugaban ƙasar ba, shi ma ya shafe shekaru ana damawa da shi a siyasar Najeriya.
Gwamnan jihar da ya fi ƙarancin shekaru a Najeriya a halin yanzu shi ne Usman Ahmed Ododo na Jihar Kogi, mai shekaru 48 a duniya.
A gefe guda kuma, gwamnonin da suka fi kowa shekaru su ne Bala Mohammed da Hope Uzodimma, waɗanda dukkansu ke da shekaru 67.
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu, yana da shekaru 74 a duniya, wanda ya sa ya fi kowane gwamna mai ci a yanzu shekaru. Tinubu ya girmi gwamnan da ya fi ƙarancin shekaru da shekara 26, sannan ya girmi gwamnonin da suka fi kowa shekaru da shekara bakwai.
Haka kuma akwai gwamnoni da dama da shekarunsu ke tsakanin shekaru 50 zuwa sama, ciki har da Seyi Makinde, Hyacinth Alia da Ahmadu Umaru Fintiri.
Wannan na nuna cewa shugabancin jihohin Naje
📌 Kaynak
Bu haber XML kaynağından derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.
Orijinal haberi oku →