Babban sifeton ƴansandan Najeriya ya umarci ƙara jami'ai a makarantun Katsina

📌 Diğer 📰 Nigeria 🕐 3 saat önce
Babban sifeton ƴansandan Najeriya ya umarci ƙara jami'ai a makarantun Katsina

Wannan shafi ne da ke kawo muku labaran abubuwan da ke faruwa a Najeriya da sauran sassan duniya, 18/06/2026

Gwamnatin ƙasar Equatorial Guinea ta yi murabus bayan gaza sauke nauyin da aka ɗora mata, kamar yadda Mataimakin Shugaban Ƙasar, Teodoro Nguema Obiang Mangue, ya bayyana.

Obiang, wanda kuma ɗa ne ga shugaban ƙasar, Teodoro Obiang Nguema Mbasogo, ya ce firaminista Manuel Osa Nsue Nsua ya miƙa takardar murabus ɗinsa da dukkan muƙarraban gwamnatin bayan sun kasa cika ko da kashi 10 cikin 100 na nauyin da aka ɗora musu.

Sai dai wata sanarwa daga jam'iyyar gwamnati ta PDGE ta fitar, ta ce shugaban ƙasar ya lura cewa gwamnatin ta gaza waje yaƙi da cin hanci da rashawa, sannan ba ta yi nasarar bunƙasa tattalin arzikin ƙasar ta hanyoyi daban-daban ba.

Shugaba Obiang, wanda ya kwashe lokaci mafi tsawo yana mulki a duniya, ya jagoranci ƙasar mai arzikin man fetur tun daga shekarar 1979.

A tsawon wannan lokaci ya ci gaba da naɗa 'yan uwansa da na kusa da shi a manyan muƙaman gwamnati.

Shugaban ya naɗa gwamnatin da ta yi murabus ne a shekarar 2024, tare da Manuel Osa Nsue Nsua a matsayin firaminista.

PDGE ta ce shugaban ƙasar bai gamsu da yadda gwamnatin da ta sauka ta gudanar da ayyukanta ba, kuma ana sa ran za a naɗa sabuwar gwamnati nan gaba kaɗan.

📌 Kaynak

Bu haber XML kaynağından derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.

Orijinal haberi oku →
📱
News AI World — Mobil uygulama
Bu haberleri 45 dilde, anlık çeviriyle cebinde. Erken erişim için Gmail adresini bırak.
← Tüm haberlere dön