Abin da muka sani kan bidiyon dandazon masu ɗauke da makamai kan babura a Najeriya

📌 Diğer 📰 Nigeria 🕐 3 saat önce
Abin da muka sani kan bidiyon dandazon masu ɗauke da makamai kan babura a Najeriya

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne a yankin Matazu da Musawa na jihar Katsina, ɗaya daga cikin jihohin da ke fama da matsalar tsaro.

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta bayanan da suka bazu a ƙasar game da wani bidiyon da ya nuna jami'in ɗansanda na ɗaga wa wasu da ake zargi da kasancewa ƴanbindiga hannu a kan titi.

Sai dai har yanzu ƴan ƙasar na ci gaba da muhawara kan bidiyon, wanda ya nuna wasu mutane a kan babura riƙe da makamai lokacin da suka iske wani abu da ya yi kama da shingen jami'an ƴansanda a wani yankin arewacin ƙasar.

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne a yankin Matazu da Musawa na jihar Katsina, ɗaya daga cikin jihohin da ke fama da matsalar tsaro.

Yankin arewa maso yammacin Najeriya ya jima yana fuskantar matsalar tsaro, inda ƴanbindiga ke addabar al'umma ta hanyar kai hare-hare da sace mutane domin neman kuɗin fansa.

A cikin bidiyon, mai tsawon ƙasa da minti ɗaya wanda ya karaɗe shafukan sada zumunta, an ga wasu jami'an ƴansanda da ke tsaye a wani wuri da ya yi kama da shingen binciken ababen hawa a kan titi.

Jami'ai biyu aka gani a cikin bidiyon sai kuma wata mota da ta yi kama da ta ƴansandan.

An ga jami'an biyu suna ɗaga hannu ga ayarin mutanen da ke kan babura, alamar sun amince musu su ci gaba da tafiya yayin da mutanen suka ci gaba da tafiya a baburansu cikin ayari.

Mutanen a kan babura kusan 40 kowane da goyo, sun riƙa wucewa riƙe da bindigogi, suna musayar ɗaga hannu da jami'an ƴansandan da ke tsaye.

Babban abin da ya janyo muhawarar shi ne yadda aka ga mutanen riƙe da makamai kuma a kan babura, wani salo da ƴanbindigar suka yi fice wajen amfani da shi.

Sannan yadda ƴansandan suka ba su damar wucewa ta kusa da su har ma suna musayar ɗaga hannu na daga cikin abubuwan da suka ɗauki hankalin masu muhawarar a shafukan sada zumunta.

Haka kuma a cikin bidiyon an ji wata murya da ke kusa da kyamarar na cewa ''duk waɗannan fa ɓarayin daji ne... ka ga wani da kakin sojoji...'', sai wasu da ke kusa da wurin suka katse shi da cewa ''kai me ya sa kake haka ne Aminu'', sai ya yi shiru.

Rundunar ƴansandan Najeriya ta musanta zargin cewa mutanen ƴanbindiga ne.

Cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ƴansandan ƙasar, CSP Anietie Okokon Edem Iniedu, ta fitar ta ce binciken da rundunar ƴansandan ƙasar ta gudanar ya nuna mutanen ƴan bijilanti ne da kuma mafarauta masu rajista da ke taimaka wa jami'an tsaro a ƙananan hukumomin Matazu da Musawa a jihar Katsina.

A cewar CSP Iniedu bidiyon ya nuna yadda kyakkyawar hulɗa ta kasance tsakanin jami'in ɗansanda da ƴan sa-kan a lokacin da suke kan hanyarsu ta zuwa wurin aiki a yankunan.

"Mutanen da aka gani a cikin bidiyon ba ƴanbindiga ba ne. Ƴan ƙungiyar bijilanti ne da kuma mafarauta masu rajista da ke tallafa wa ayyukan

📌 Kaynak

Bu haber XML kaynağından derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.

Orijinal haberi oku →
📱
News AI World — Mobil uygulama
Bu haberleri 45 dilde, anlık çeviriyle cebinde. Erken erişim için Gmail adresini bırak.
← Tüm haberlere dön