Atiku da Kwankwaso: Abokan tafiyar siyasa da suka raba gari

📌 Diğer 📰 BBC Hausa 🕐 10 saat önce
Atiku da Kwankwaso: Abokan tafiyar siyasa da suka raba gari

A watannin baya ne magoya bayan ɓangarorin biyu suka fara murna bayan jagororin siyasar biyu sun dunƙule a jam'iyyar ADC domin fuskantar APC, amma sai auren ya ƙi daɗi, inda suka rabu bayan lokaci kaɗan.

A daidai lokacin da ake cigaba da shirye-shiryen babban zaɓen 2027, siyasar arewacin Najeriya ta ɗauki zafi ne kan muhawarar da ake tafkawa game da Atiku Abubakar da Rabiu Musa Kwankwanso.

Magoya bayan fitattun ƴan siyasar na arewa suna ta musayar yawu ne kan wane ne ya fi girma da ƙarfi da tarin masoya da ma gogewa a siyasar, da kuma tunanin wanda ya fi girma a siyasar ƙasar.

A watannin baya ne magoya bayan ɓangarorin biyu suka fara murna bayan jagororin siyasar biyu sun dunƙule a jam'iyyar ADC domin fuskantar APC, amma sai auren ya ƙi daɗi, inda suka rabu bayan lokaci kaɗan.

Atiku Abubakar dai shi ne ɗan takarar shugaban ƙasa a jam'iyyar ADC, inda ya samu jimillar ƙuri'a 1,846,370, inda ya kayar da sauran ƴan takara biyu - Rotimi Amaechi wada ya samu jimillar ƙuri'u 504,117, sai Muhammed Hayatudden a matsayi na uku da jimillar ƙuri'u 177,120.

Shi kuma Rabiu Musa Kwankwanso shi ne ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa a jam'iyyar NDC, ina zai mara wa Peter Obi baya domin fafatawa da jam'iyyar APC mai mulki da ADC da sauran jam'iyyu a babban zaɓen na 2027.

Amma me ya sa magoya bayan ƴansiyasar biyu suke takun-saƙa? kuma me yake haɗa su?

Dangantakar siyasa tsakanin Atiku Abubakar da Rabiu Musa Kwankwaso ta daɗe, domin sun shafe sama da shekara 30 suna gwagwarmayar siyasa, lamarin da ya sa ake tunanin ya kamata su kasance makusantan juna a siyasa..

Duk da cewa a wasu lokuta sun kasance a jam'iyyu daban-daban ko kuma sun kara da juna a zaɓe, asalinsu na siyasa ya samo asali ne daga tafiya guda ƙarƙashin marigayi Shehu Musa Yar'Adua.

A zamanin mulkin soji na Janar Ibrahim Babangida ne da aka fara shirye-shiryen komawa dimokuraɗiyya ta Jamhuriya ta uku, Shehu Musa Yar'Adua ya kafa ƙungiyar siyasa ta People's Front of Nigeria, wadda ta kasance ɗaya daga cikin ƙungiyoyin siyasa mafi ƙarfi a wancan lokaci.

Atiku da Kwankwaso dukkansu sun kasance cikin fitattun mambobin wannan ƙungiya tare da wasu ƴan siyasa, waɗanda yawancinsu daga baya suka mamaye siyasar Najeriya.

A lokacin an samu cikas saboda gwamnati ta ƙi yi wa People's Front rajista a matsayin jam'iyyar siyasa, wanda hakan ya sa mambobinta da dama suka shiga jam'iyyar SDP domin shiga zaɓen 1992.

A zaɓen shekarar 1992, Kwankwaso ya lashe kujerar majalisar wakilai, inda ya zama mataimakin shugaban majalisar. A gefe guda kuma, Atiku ya fara da takarar gwamna sannan daga baya ya nemi tikitin takarar shugaban ƙasa na SDP a shekarar 1993, inda ya fafata takarar fitar da gwani, amma Abiola ya doke shi.

Yanzu za ku iya samun labaran BBC Hausa kai-tsaye a wayoyinku.

Bayan rushewar Jamhuriya ta uku saka

📌 Kaynak

Bu özet BBC Hausa kaynağından otomatik derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.

Orijinal haberi oku →
← Tüm haberlere dön