Dalilai uku da suka sa hare-hare ƴan bindiga ke ta'azzara a kudancin Najeriya
A farkon wannan shekarar ne aka ɗaure Simon Ekpa a ƙasar Finland saboda kama shi da laifin ta'addanci.
A Najeriya, masana na tattaunawa game da yadda hare-haren ƴanbindiga suka fara ɗaukar sabon salo, musamman inda garkuwa da mutane, ciki har da ɗalibai ke neman zama ruwan dare a kudancin ƙaar.
Najeriya dai ta daɗe tana fama da rikice-rikice da suka haɗa da garkuwa da mutane da kashe-kashe da sauran matsalolin tsaro.
Duk da cewa asalin garkuwa da mutane daga kudancin ƙasar ya samo asali, lamarin ya yi ƙamarin gaske a arewacin ƙasar, inda har ake tunanin matsalar ce da ta samo asali daga yankin ce.
Sai dai ko a lokacin da garkuwa da mutanen ke tashe a kudancin ƙasar, mahara sun fi ɗaukar manyan mutane da ko iyalansu, ko kuma ma'aikatan manyan kamfanoni da suka san za a samu kuɗi, duk da cewa sukan ɗauki ɗaiɗaikun mutane marasa ƙarfi.
Saɓanin haka ne a arewacin Najeriya, inda mahara sukan sace mutane na kan mai uwa da wabi, har a kan samu lokacin da ake sace ƙauye baki ɗaya, ko kuma a sace manoma a mutane waɗanda talakawa futik.
Wata matsalar da ta yi ƙamari a kudancin Najeriya ita ce matsalar ƴan aware a yankin kudu maso gabas, inda aka samu ɓatagari da suke garkuwa da mutane da kashe-kashe.
Rikicin neman ɓallewa a Najeriya ya samo asali ne daga yunƙurin kafa ƙasar Biafra, wanda ya janyo yaƙin basasar ƙasar kimanin shekara 60 da suka gabata, wanda ya yi ajalin sama da mutum miliyan 2.
An zargi ƙungiyar ESN, kamar yadda ake kiranta a baya da zargin garkuwa da fararen hula da jami'an tsaro a jihohin kudu maso gabas, inda har suke tursasa mutane da dama zaman dole a wasu garuruwan yankin a ranar Litinin, lamarin da ke haifar da ƙuncin tattalin arziki.
Akwai ƴanbindiga da suka fi addabar arewa maso yamma, sai mahara masu iƙirarin jihadi da suka fi addabar arewa maso gabas, akwai rikicin makiyaya da manoma a tsakiyar ƙasar, sai kuma rikicin masu yunƙurin ɓallewa daga ƙasar a kudu maso gabas.
Wannan ya sa aiki yake yawa kan sojojin ƙasar kusan 400,000 da ƴansanda 370,000.
A farkon wannan shekarar ne aka ɗaure Simon Ekpa a ƙasar Finland saboda kama shi da laifin ta'addanci.
BBC ta tattauna da Kabiru Adamu, shugaban Kamfanin Beacon Security and Innovations Limited, kuma mai sharhi kan harkokin tsaro, inda ya zayyano wasu abubuwa uku da ya ce su ne dalilan da suka sa matsalar take ƙamari a kudu
Dr Kabiru Adamu ya ce ba abin mamaki ganin yadda maharan suke ƙoƙarin kutsawa kudancin Najeriya, domin a cewarsa, dama tun asali suna da niyyar samun wurin zama a yankunan bakin teku.
''Kasancewar kudancin Najeriya na cikin taswirar da ƴanbindiga suka tsara, bayanan da suka fito na yadda suke tsara manufarsu, suna da burin kama wuraren da ke bakin teku."
Masani
📌 Kaynak
Bu özet BBC Hausa kaynağından otomatik derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.
Orijinal haberi oku →