Yadda aka sace ɗalibai sama da 2,000 a Najeriya tsakanin 2014 zuwa 2026

📌 Diğer 📰 BBC Hausa 🕐 1 gün önce
Yadda aka sace ɗalibai sama da 2,000 a Najeriya tsakanin 2014 zuwa 2026

Ana fara buɗe ido da garkuwa da ɗalibai ƴan makaranta ne a zamanin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan, inda mayaƙan Boko Haram suka sace ƴan makarantar Chibok.

A Najeriya, ana cigaba da tattaunawa kan sace ɗaliban wasu makarantu a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya da kuma jihar Oyo da ke kudu maso yammacin kasar.

A jihar Borno, bayanai sun ce gomman ɗalibai sun ɓata a wasu makarantu da ke cikin haraba guda, bayan wani hari da 'yan Boko Haram suka kai garin Mussa na ƙaramar hukumar Askira Uba.

A jihar ta Oyo kuma, hukumomi ne suka tabbatar cewa ƴanbindiga sun kai hari kan wasu makarantu guda biyu a garin Ahoro-Esinle, inda suka hallaka wani malami kuma suka sace ɗalibai.

Lamarin ya ɗauki hankali matuƙa gaya, inda har malaman makaranta suka yi zanga-zanga tare da rufe makarantu, suna masu kira ga gwamnati da ta ceto yaran, sannan ta ba su tabbacin tsaro.

Ana fara buɗe ido da garkuwa da ɗalibai ƴan makaranta ne a zamanin tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan, inda mayaƙan Boko Haram suka sace ƴan makarantar Chibok.

Tun daga lokacin ne mayaƙan Boko Haram da ƴanbindiga suka cigaba da sace ɗalibai, inda zuwa yanzu aka sace ɗalibai a makarantu aƙalla 25 a jihohi daba-daban na Najeriya, tare da sace ɗalibai aƙalla 2,000.

BBC ta tattara bayanan wasu makarantu da aka sace, musamman waɗanda suka fi jan hankali ta hanyar tattara rahotannin jaridu irin su ICiR da Premium Times.

A ranar 14 ga watan Afrilun 2014 ne mayaƙan Boko Haram suka kai wani hari makarantar sakandaren mata da ke Chibok a jihar Borno, inda suka sace ɗalibai masu yawa.

Mayaƙan ɗauke da manyan bindigoyi sun shiga garin da tsakar dare suka tashi mazauna da ƙarar harbi kafin su kutsa cikin ɗakunan kwanan ɗalibai suka loda su a motoci sannan suka yi awon gaba da ƴanmata 276.

Wannan hari shi ne irin sa na farko da mahara suka sace ɗalibai a makaranta, batun satar ɗaliban ya ja hankalin duniya.

Hakan ya sa ƙasashen duniya suka yi ta sukar gwamnatin Najeriya ta wancan lokacin bisa rashin ɗaukar mataki, inda aka fara gangamin #BringBackOurGirl a shafin Twitter wanda ke nufin 'A dawo da ƴaƴanmu mata'. An dai samu nasarar ceto da yawa daga cikin su.

A watan Mayun shekarar 2017, ƴanbindiga suka sace ɗalibai guda shida daga makarantar Lagos State Model College da ke garin Igbonla a jihar Legas.

An sake ɗaliban bayan kimanin kwana 65 a hannun masu garkuwar.

A zamanin tsohon shugaban ƙasa marigayi Muhammadu Buhari, a daidai lokacin da yake ƙoƙarin ceto ɗaliban Chibok, sai kwatsam a watan Fabrairun 2018 ƴan Boko Haram kai hari makarantar mata da ke garin Dapchi na jihar Yobe sannan suka sace ɗalibai 110.

Lamarin ya faru ne kusan shekara huɗu bayan sace ƴanmatan makarantar Chibok.

An saki 104 daga cikinsu a watan Maris na 2018 yayin da biyar

📌 Kaynak

Bu özet BBC Hausa kaynağından otomatik derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.

Orijinal haberi oku →
← Tüm haberlere dön