Me Inec za ta yi kan ƴantakara fiye da ɗaya da jam'iyyun adawa suka tsayar?
Wa'adin da hukumar zaɓen Najeriya ta sanya ga jam'iyyun siyasa su kammala gudanar da zaɓen cikin gida sannan kuma su miƙa sunayen ƴan takararsu da za su tsaya musu takarar zaɓen 2027, ya wuce.
Wa'adin da hukumar zaɓen Najeriya ta sanya ga jam'iyyun siyasa su kammala gudanar da zaɓen cikin gida sannan kuma su miƙa sunayen ƴan takararsu da za su tsaya musu takarar zaɓen 2027, ya wuce.
Duk da cewa dai jadawalin zaɓen 2027 da hukumar ta Inec ta fitar har yanzu wani abu ne da ke gaban kotu, dukkannin jam'iyyun sun fitar da sunayen waɗanda za su tsaya musu takarar shugabancin ƙasa.
Bugu da ƙari, duk da cewa jam'iyyu sun kammala zaɓen fidda gwani, har yanzu akwai batutuwa masu sarƙaƙiya a jam'iyyu da dama.
Saboda haka yanzu tambayar da ake ita ce mene ne abu na gaba ga waɗannan jam'iyyu da ƴan takararsu musamman waɗanda suka tsayar da guda biyu?
Da dama dai daga cikin jam'iyyun adawa sun dare zuwa gida biyu inda kowane ɓangare ya fitar da nasa ƴan takarar, yanzu mene ne makomar ƴan takarar?
Jam'iyyar hamayya ta PDP ita ce gaba wajen rabuwar kai, inda ƴan takara guda biyu suka fito a matsayin ƴan takarar shugabancin ƙasa.
Ɓangaren da Kabiru Turaki ke jagoranta ya fito da tsohon shugaban Najeriya, Goodluck Jonathan a matsayin ɗan takarar shugabancin jam'iyyar a 2027.
Shi ma tsagin da Abdulrahman Mohammed ke shugabanci wanda ke samun goyon bayan ministan Abuja, Nyesom Wike, ya tsayar sanata Sandy Onor.
Goodluck Jonathan dai har yanzu bai ce uffan ba dangane da ko ya amince da zai tsaya ko kuma bai amince ba.
To amma kuma shi sanata Onor ya amince da tsayawa takarar inda ya ce zai yi gangamin neman a zaɓe shi ba tare da ɓata lokaci ba.
Daga ƙarshe dai hukumar zaɓe ta Inec ce za ta faɗi wane ne halastaccen dan takara bisa la'akari da shari'o'in kotu duk da cewa akwai yiwuwar batun ya sake komawa ga kotu domin tantancewa.
Ita ma jam'iyyar hamayya ta ADC na da mutum biyu da suka fito takarar shugaban ƙasar kamar yadda take da ɓangarori guda biyu.
Ɓangaren tsohon ɗantakarar shugaban ƙasa a 2023, Ibeh Kachikuwu ya tsayar da Kachikun a matsayin ɗan takara, inda shi kuma ɓangaren shugaban jam'iyyar, sanata David Mark ya tsayar da tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar.
Ita ma dai wannan jumurɗa kotu ce kawai za ta iya warware ta a nan gaba.
Kamar sauran jam'iyyun na adawa a Najeriya, ita ma jam'iyyar Labour Party, LP mutum biyu ne suka fito daga cikinta a matsayin masu neman kujerar shugaban Najeriya a zaɓen 2027.
Dukkannin ɓangarori biyu da suke taƙaddama a jagorancin jam'iyyar sun tsayar da ƴan takararsu, inda ɓangaren Nenadi Usman ya sanar da Chibuzo Okereke a matsayin ɗan takara, shi kuma ɓangaren Julius Abure ya sanar da sunan Kennedy Ahanotu.
A yanzu dai za a iya cewa babu wata shari'a da ake yi kan jagoranci a jam'iyyar LP to
📌 Kaynak
Bu özet BBC Hausa kaynağından otomatik derlenmiştir. Tamamı için orijinal habere gidin.
Orijinal haberi oku →